‘Yan ta’adda sun hallaka mutane 3 a titin Yawuri zuwa Koko, bayan da suka yi barin wuta a kan titin.
Rahotanni sun tabbatar da cewa, ‘yan ta’addan sun fito ne daga Rijau a jihar Neja, kuma suka tare masu tafiya daga Neja zuwa Sokoto.
Wani ganau ya bayar da labarin yadda suka yi sa’a daya suna cin karensu babu babbaka, kuma suka shiga kauyen Shanga inda suka saci shanu.
Tun a ranar Asabar, ‘yan bindigar suka tare titin birnin Yauri zuwa karamar hukumar Koko dake jihar Kebbi.