Rahotanni daga jihar Edo da ke kudu maso kudancin Najeriya na cewa mutum uku sun mutu sakamakon rikicin da ke da alaka da neman shugabanci a karamar hukumar Uhunmwonde.
Kamfanin dillancin labaran Najeriya, NAN, ya rawaito cewa lamarin ya faru ne a kauyen Uselu-Nahor ranar Laraba.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Katongs Bello, ya tabbatar da aukuwar lamarin sai dai bai yi karin bayani ba.
Kamfanin dillancin labarai na Æ™asa (NAN) ya rawaito cewa, wasu ‘yan bindiga ne suka kai hari kan mutanen, kuma daya daga cikin wadanda aka kashe jami’in tsaro ne da ke aiki a Ahor Kara.
Mutanen suna karbar kudin fakin na motoci lokacin da ‘yan bindigar suka kai mutu harin inda suka kashe mutum uku nan take.
Bayanai sun nuna cewa rikicin yana da nasaba da rikicin shugabanci da ya ki ci ya ki cinyewa a kauyen.