fidelitybank

Mutane 3 sun mutu a bikin hawa Kaho a kasar Sifaniya

Date:

Mutum uku ne suka mutu cikin kwana guda sakamakon raunukan da suka ji a bikin hawan kaho da aka gudanar a gabashin kasar Sifaniya.

Lamarin ya faru ne a yankin Valencia, inda aka gudanar da bukukuwan hawan kahon, lokacin da wasu manyan bijimai suka kwato tare da nufowa cikin gari, yayin da mutane suka rika gudu don tseratar da rayukansu.

kungiyoyin kare hakkin dabbobi dai sun sha yin korafe-korafe, game da hatsarin da ke tattare da wannan wasa ga mutane da ma su kansu dabbobin.

Suna masu cewa mutum 20 ne suka mutu a yankin cikin shekara takwas sakamakon wannan wasa.

Duka mutane ukun da suka mutu, sun samu munanan raunuka ne lokacin da lamarin ya faru makonni biyu da suka gabata. In ji BBC.

Daya daga cikinsu ya gamu da ajalinsa ne lokacin da wani bijimi ya yi awon-gaba da shi yayin da ya same shi tseye a gefen wani gini.

Sannan akwai wani mai shekarar 50 da wani katon bijimi ya soka masa kaho a cikinsa, a garin Meliana da ke arewacin Valencia

Sai kuma wani Bafaranshe mai yawon bude-ido da shi ma ya mutu a ranar Litinin sakamakon raunin da bijimin ya ji masa lokacin da ya kwada shi kan wani katon dutse.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp