fidelitybank

Mutane 27 sun mutu bayan kifewar Kwale-Kwale a Kwara

Date:

Mutum 27 ne suka rasu bayan da kwale-kwalensu ya kife a karamar hukumar Kaiama na jihar Kwara.

Rahotanni sun bayyana cewa fasinjojin na kan hanyar su ne ta komawa gida daga kasuwa a jihar Neja, lokacin da jirginsu ya nitse.

Wani da ya tsira daga hatsarin, ya ce lamarin ya faru ne sakamakon ɗaukar kaya fiye da kima, kamar yadda gidan talabijin na Channels a Najeriya ya ruwaito.

Ya ce iska mai ƙarfi da ta taso musu – ita ma ta taimaka wajen kifar da kwale-kwalen, duk da cewa bai bayyana adadin mutanen da ke cikin jirgin ba.

Shugaban karamar hukumar ta Kaiama, Abdullahi Danladi, wanda ya jagoranci tawagar gwamnatin jihar don zuwa ta’aziyya ga iyalan waɗanda lamarin ya shafa, ya ce gwamnati ba za ta ci gaba da lamuntar samun hatsuran kwale-kwale da ake yi ba a kowace shekara.

Ya sanar da shirin kafa wani kwamitin da zai ɗabbaka saka rigunan kariya da hana tafiye-tafiye cikin dare da kuma aiwatar da sauran matakai na tsaro.

Hatsarin jirgin ruwan na zuwa ne watanni bakwai bayan samun irinsa da ya lakume rayukan mutane 100 a yankin.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...

Buhari ya ban umarni na kula da Talakawan Najeriya – Peter Obi

Jagorar jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya ce,...

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...
X whatsapp