fidelitybank

Mutane 26,800 ke mutuwa duk shekara sanadiyar taba Sigari a Najeriya

Date:

Gwamnatin Najeriya ta ce mutane 26,800 ke mutuwa a duk shekara, a sanadiyyar cututtukan da suka shafi sinadarin Tobacco, yayin da ƴan ƙasar miliyan 4.5 daga shekara 15 zuwa sama ne ke tu’ammali da sinadarin.

Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwar da hukumar kare masu amfani da kayayyaki ta ƙasar ta fitar a ranar Litinin.

Muƙaddashin hukumar, Adamu Abdullahi, ya bayyana hakan ne a wajen ƙaddamar da wani shirin daƙile amfani da sinadarin na Tobacco wanda ke ƙunshe a taba sigari da wasu abubuwa.

Shirin da aka sanya wa suna ‘kada ka ƙona makomarka’.

Adamu ya ce shirin na fatan magance ƙaruwar da ake samu na amfani da kayayyakin da ke ɗauke da sinadarin a tsakanin masu tasowa da kuma masu ƙarancin shekaru.

Inda ya ƙara da cewa shirin na kuma neman magance matsalolin da hakan ke janyo wa ga al’umma baki ɗaya.

Shugaban ya kuma jaddada muhimmancin samun ƙoshin lafiya, wanda ta haɗa da lafiyar gangar jiki da ta ƙwaƙwalwa da ta kuma walwala.

Adamu ya kuma nuna muhimmancin haɗa ƙarfi waje guda domin samar da manyan gobe masu ƙoshin lafiya.

Ya bayyana wasu daga cikin illolin tu’ammali da sinadarin tobacco ga matasa da suka haɗa da illa kan ƙwaƙalwa da hanyoyin numfashi da kuma yadda rayuwa ke ta’allaka da sinadarin nicotine.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp