Gwamnatin Najeriya ta ce mutane 26,800 ke mutuwa a duk shekara, a sanadiyyar cututtukan da suka shafi sinadarin Tobacco, yayin da ƴan ƙasar miliyan 4.5 daga shekara 15 zuwa sama ne ke tu’ammali da sinadarin.
Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwar da hukumar kare masu amfani da kayayyaki ta ƙasar ta fitar a ranar Litinin.
Muƙaddashin hukumar, Adamu Abdullahi, ya bayyana hakan ne a wajen ƙaddamar da wani shirin daƙile amfani da sinadarin na Tobacco wanda ke ƙunshe a taba sigari da wasu abubuwa.
Shirin da aka sanya wa suna ‘kada ka ƙona makomarka’.
Adamu ya ce shirin na fatan magance ƙaruwar da ake samu na amfani da kayayyakin da ke ɗauke da sinadarin a tsakanin masu tasowa da kuma masu ƙarancin shekaru.
Inda ya ƙara da cewa shirin na kuma neman magance matsalolin da hakan ke janyo wa ga al’umma baki ɗaya.
Shugaban ya kuma jaddada muhimmancin samun ƙoshin lafiya, wanda ta haɗa da lafiyar gangar jiki da ta ƙwaƙwalwa da ta kuma walwala.
Adamu ya kuma nuna muhimmancin haɗa ƙarfi waje guda domin samar da manyan gobe masu ƙoshin lafiya.
Ya bayyana wasu daga cikin illolin tu’ammali da sinadarin tobacco ga matasa da suka haɗa da illa kan ƙwaƙalwa da hanyoyin numfashi da kuma yadda rayuwa ke ta’allaka da sinadarin nicotine.