Yayin da ake ci gaba da laluɓe, hukumomi sun tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 23 sanadiyyar hatsarin jirgin ruwa a ƙaramar hukumar Yauri ta jihar Kebbi.
An ruwaito cewa mutane da dama ne kuma suka ɓata waɗanda ake ci gaba da nema.
Waɗanda lamarin ya shafa sun kasance ƴan kasuwa da suka fito daga jihar Neja zuwa Yauri domin cin kasuwa, da ke ci mako-mako.
Wannan dai ya kasance hatsarin jirgin ruwa na uku da aka samu a ƴan watannin nan, inda wanda ya faru a baya-bayan nan ya janyo mutuwar gwamman mutane.