Kwamitin binciken fashewar tankar mai na jihar Jigawa ya ce, mutane 209 ne suka rasu, sannan mutum 99 suka jikkata, bayan kadarorin miliyoyin naira da aka rasa a ibtila’in wanda ya auku a ranar 14 ga Oktoba a garin Majiya da ke jihar ta Jigawa.
Kwamitin, wanda Hafizu Inuwa ya jagoranta ne ya bayyana hakan a lokacin da yake miƙa rahoton bincikensa ga gwamna Umar Namadi a ranar Laraba kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Rahoton kwamitin ya kuma nuna cewa har yanzu akwai mutum 38 da suke jinya a asibiti a sanadiyar lamarin wanda ya shafi iyalai 167.
Kwamitin ya kuma bayar da shawarar a riƙa kiyaye wajen sufurin man fetur, sannan ya buƙaci a samar da sashen kula da tashin hankali a asibitoci, sannan a kafa hukumar kula sufuri domin tabbatar da bin dokar tuƙi.
A nasa ɓangaren, gwamnan jihar ya yaba wa mambobin kwamitin bisa aikin da suka yi, sannan ya ce a shirye suke su aiwatar da shawarwarin da kwamitin ya bayar.