Gwamnan birnin Makka Yarima Khalid Al-Faisal ya mika wa babban mai kula da masallacin Ka’aba Dr. Saleh bin Zain-ul-Abidin Al-Shaibi sabuwar rigar dakin Ka’aba da aka fi sani da Kiswa a madadin Sarkin Saudiyya Salman bin Abdul’aziz
Jaridar Saudi Gazzet ta ruwaito cewa Dr. Saleh bin Zain-ul-Abidin Al-Shaibi tare da rakiyar babban shugaban masallatai biyu mafiya daraja Sheikh Abdurrahman Al-Sudaise sun karbi sabuwar rigar a wata kwarya-kwaryar liyafa da aka shirya a birnin Muna.
A wani bangare na shirye-shiryen sabunta wa dakin Ka’aba riga da za a yi ranar daya ga watan Muharram na sabuwar shekarar hijira ta 1444.
Ana bukatar akalla mutum 200 domin saka wa dakin Ka’aba sabuwar rigar ta Kiswa.