fidelitybank

Mutane 20 sun rasa ransu a rikicin Taraba

Date:

Akalla mutane ashirin ne suka mutu sakamakon wani rikicin kabilanci da ya barke tsakanin kabilun Wurkunawa da kuma Karimjo a Karamar Hukumar Karim Lamido ta jihar Taraba.

An kuma kona gidaje da dama da asarar dukiya mai dimbin yawa.

Tashin hankalin ya samo asali ne kan batun sarautar gargajiya a yankin.

A cikin makon da ya gabata ne gwamnan jihar ta Taraba Darius Ishaku ya bai wa Alhaji Yakubu Abubakar Haruna sanda a matsayin sabon sarki a masarautar Wurkum da ke Karamar Hukumar Karim Lamido a jihar Taraba.

An nada sarkin ne bayan rasuwar mahaifinsa da ya shafe shekara 47 yana mulki.

BBC ta tattauna da dukkan bangarorin da ke rikici da junan kuma shugaban kungiyar ci-gaban al’ummar Wurkum na duniya Wilfred Habuba Yambakam Kwanchi, ya ce dukkan bangarori sun yi asara a rikicin.

“An dan samu zaman lafiya a cikin gari amma a kauyuka inda Wurkunawa suke har yanzu ana ta’adi, ana kona gidajen mutane sannan an kashe wasu yara.

Abincin gidaje da dabbobinsu ma duk an tafi da su, an yi asarar rayuka kuma a halin yanzu ba za mu iya cewa ga adadin mutanen ba amma sun fi goma sha biyar” a cewar Wilfred.

Ya kara da cewa gwamnati ta tura jami’an tsaro a yankin da lamarin ya auku.

Sannan yayi zargin cewa tun ranar da aka nada sabon sarki na garin wanda dan kabilar Wurkunawa ne sai ‘yan kabilar Karimjo suka fara kone-konen tayoyi a cikin garin Karim Lamido.

Wilfred Habuba ya ce dama masarautar ta Wurkunawa ce sannan babu batun takara kan masarautar daga dukkan kabilu da ke yankin.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaÆ™i – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama É—an kasar China da zargin kai wa Æ´an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp