fidelitybank

Mutane 20 sun rasa ransu a rikicin Taraba

Date:

Akalla mutane ashirin ne suka mutu sakamakon wani rikicin kabilanci da ya barke tsakanin kabilun Wurkunawa da kuma Karimjo a Karamar Hukumar Karim Lamido ta jihar Taraba.

An kuma kona gidaje da dama da asarar dukiya mai dimbin yawa.

Tashin hankalin ya samo asali ne kan batun sarautar gargajiya a yankin.

A cikin makon da ya gabata ne gwamnan jihar ta Taraba Darius Ishaku ya bai wa Alhaji Yakubu Abubakar Haruna sanda a matsayin sabon sarki a masarautar Wurkum da ke Karamar Hukumar Karim Lamido a jihar Taraba.

An nada sarkin ne bayan rasuwar mahaifinsa da ya shafe shekara 47 yana mulki.

BBC ta tattauna da dukkan bangarorin da ke rikici da junan kuma shugaban kungiyar ci-gaban al’ummar Wurkum na duniya Wilfred Habuba Yambakam Kwanchi, ya ce dukkan bangarori sun yi asara a rikicin.

“An dan samu zaman lafiya a cikin gari amma a kauyuka inda Wurkunawa suke har yanzu ana ta’adi, ana kona gidajen mutane sannan an kashe wasu yara.

Abincin gidaje da dabbobinsu ma duk an tafi da su, an yi asarar rayuka kuma a halin yanzu ba za mu iya cewa ga adadin mutanen ba amma sun fi goma sha biyar” a cewar Wilfred.

Ya kara da cewa gwamnati ta tura jami’an tsaro a yankin da lamarin ya auku.

Sannan yayi zargin cewa tun ranar da aka nada sabon sarki na garin wanda dan kabilar Wurkunawa ne sai ‘yan kabilar Karimjo suka fara kone-konen tayoyi a cikin garin Karim Lamido.

Wilfred Habuba ya ce dama masarautar ta Wurkunawa ce sannan babu batun takara kan masarautar daga dukkan kabilu da ke yankin.

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp