fidelitybank

Mutane 20 sun Mutu: Sojojin Amurka sun tallafa an farmaki ‘yan Boko Haram

Date:

Sama da ‘yan kungiyar Boko Haram da na Islamic State of West Africa (ISWAP) 20 ne a ka tabbatar da cewa an kashe su a wani samamen da sojojin hadin gwiwa na sama da na kasa da su ka yi na tsawon mako guda da sojojin Najeriya da na Nijar a tafkin Chadi.

A cewar wata sanarwa a ranar Juma’a, 24 ga watan Disamba ta hannun rundunar hadin gwiwa ta Multinational Joint Task Force (MNJTF) reshen 4 mai shelkwata a yankin Diffa da ke Kudu maso Gabashin Nijar, an kashe sojoji shida daga Najeriya da Nijar yayin farmakin da jiragen yaki da kuma abokan Amurka ke marawa baya.

Shirin na MNJTF na tsawon mako uku mai suna Sharan Fage, wanda a ka gudanar da shi ne a matakai biyu a yankin tafkin Chadi na Najeriya tsakanin 1 zuwa 21 ga watan Disamba.

Akalla mahara 22 ne su ka mutu a harin yayin da sojojin Nijar da na Najeriya 23 suka samu raunuka tare da lalata motoci biyu.

Sanarwar ta kara da cewa sojojin na hadin gwiwa sun fuskanci hare-hare daga da harin gaba da wata mota kirar bama-bamai (VBIED) ta kai.

A ranar 14 ga watan Disamba, kungiyar ISWAP ta yi ikirarin kai harin kunar bakin wake da a ka kai da mota a kan sojojin Najeriya da na Nijar kwanaki kadan da suka gabata.

An gudanar da aikin kashi na farko a garin Malam Fatori kusa da gabar tafkin Chadi. Ya hada da katangar garin, domin tallafawa kokarin sake tsugunar da su.

Kashi na biyu ya shafi ayyuka a Arege, Gashigar, Asaga, da Kamagunma.

Har ila yau, aikin ya yi sanadin kwatowa tare da lalata motoci, da babura da kuma makaman atilare da ke nuni zuwa birnin Diffa.

 

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp