Mutane kusan 20 suka mutu a Morocco, bayan sun sha wata barasa mai guba a wani kantin gefen titi da ke birnin Ksar el-Kebir na arewacin kasar.
An kuma kai wasu gommai zuwa asibiti cikin mawuyacin hali, inda mutum biyu ke kwance a dakin kula da masu matsananciyar jinya.
Hukumomi sun kama wani mutum mai shekara 48 bisa zargin hannu a lamarin. Yayin da ‘yan sanda suka ce sun gano kimanin lita 50 ta ruwan barasar a shagonsa.
Haramun ne sayar da barasa a kasar Moroko, sai dai rahotanni sun ce sau da yawa ana sayar da gidajen cin abinci da kantuna a fakaice. In ji BBC.
A watan Agusta, mutum takwas ne aka ba da rahoton mutuwarsu bayan sun sha gurbatacciyar barasa a yankin Oriental na arewacin kasar.
Kimanin mutum 20 kuma sun mutu a watan Yulin bara a irin wannan lamari da ya faru a Oujda, da ke gabashin Moroko.