Wasu mutane sha takwas sun tsallake rijiya da baya, a ranar Alhamis yayin da wata mota kirar Toyota Hiace mai kujeru 18 ta kama wuta a kan hanyar ta.
Lamarin da ya afku a kauyen Koko Araromi, daura da titin Ajase Ipo, a jihar Kwara, ya sa masu ababen hawa da dama suka makale.
Motar da aka ce ta na kan hanyar zuwa Osdogbo a jihar Osun ta kama wuta da misalin karfe 10:57 na safe a kan hanyar.
Duk da cewa ba a samu asarar rai ba yayin da fasinjojin suka yi gaggawar sauka daga motar bas din, duk da haka kayayyakinsu da jakunansu sun kone kurmus.
Kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) a jihar Jonathan Owoade, ya tabbatar wa Aminiya faruwar lamarin a wata tattaunawa ta wayar tarho.
Owoade wanda ya danganta lamarin da kwararar mai daga motar ya ce, “Hukumar kula da kiyaye hadura ta kasa ta dakatar da motocin da ke zuwa na wasu mintuna saboda tsananin gobarar.”