fidelitybank

Mutane 18 sun mutu a titin Bauchi

Date:

Mutum aƙalla 18 ne suka ƙone ƙurmus sakamakon wani hatsarin mota da ya afku a Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi, inda motar bas ta yi taho-mu-gama da tirela ranar Laraba.

Kwamandan yanki na hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa, Yusuf Abdullahi, ya ce hatsarin ya faru ne a ƙauyen Narbodo, kamar yadda kamfanin labarai na NAN ya ruwaito cewa. Kwamandan ya ce, hatsarin ya ƙunshi motar bas ƙirar Toyota Hiace da kuma babbar mota, wadda mutum uku da ke cikinta ba su ji ko ƙwazane ba.

A cewarsa, lamarin ya faru da misalin ƙarfe 4:40 na yamma, kuma jami’an hukumar sun isa wurin cikin minti bakwai da faruwarsa.

Ya ɗora alhakin hatsarin kan gudun wuce sa’a wanda ya haddasa motocin biyu suka yi karo da juna.

“Mutum 21 ne abin ya ritsa da su kuma akwai manya 18 da yara uku. !8 ɗin suna cikin bas ɗin kuma sun ƙone ƙurmus bayan ta kama da wuta sakamakon karon da ta yi da tirelar,” in ji shi.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp