fidelitybank

Mutane 18 sun mutu a titin Bauchi

Date:

Mutum aƙalla 18 ne suka ƙone ƙurmus sakamakon wani hatsarin mota da ya afku a Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi, inda motar bas ta yi taho-mu-gama da tirela ranar Laraba.

Kwamandan yanki na hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa, Yusuf Abdullahi, ya ce hatsarin ya faru ne a ƙauyen Narbodo, kamar yadda kamfanin labarai na NAN ya ruwaito cewa. Kwamandan ya ce, hatsarin ya ƙunshi motar bas ƙirar Toyota Hiace da kuma babbar mota, wadda mutum uku da ke cikinta ba su ji ko ƙwazane ba.

A cewarsa, lamarin ya faru da misalin ƙarfe 4:40 na yamma, kuma jami’an hukumar sun isa wurin cikin minti bakwai da faruwarsa.

Ya ɗora alhakin hatsarin kan gudun wuce sa’a wanda ya haddasa motocin biyu suka yi karo da juna.

“Mutum 21 ne abin ya ritsa da su kuma akwai manya 18 da yara uku. !8 ɗin suna cikin bas ɗin kuma sun ƙone ƙurmus bayan ta kama da wuta sakamakon karon da ta yi da tirelar,” in ji shi.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...
X whatsapp