fidelitybank

Mutane 18 ne suka mutu a Borno yayin da bam ya tashi da su a taron biki

Date:

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar Borno (SEMA) ta ce mutum 18 ne suka mutu a harin bom da wasu ‘yan ƙunan ɓakin wake suka tayar a wurin taron biki ranar Asabar a Gwoza da ke jihar.

Rahotonni sun ce fiye da mutum 30 ne suka samu munanan raunuka a harin, wanda ya kasance ɗaya daga cikin mafiya muni a baya-bayan nan.

Babban daraktan hukumar, Barkindo Saidu ne ya tabbatar da haka, yana mai cewa a kan idonsa bom na farko ya tashi.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar, NAN ya ruwaito shi yana cewa “A gaban idona, da misalin ƙarfe 3:00 na rana, bom na farko ya tashi a Gwoza, wanda wata mace ta tayar bayan ta kutsa cikin taron bikin”.

Bayan tashin bom na farko, wanda ya jikkata fiye da mutum 30, tare da kashe wasu, sai na biyu ya sake tashi a kusa da babban asibitin yankin, in ji Barkindo Saidu.

”A yayin da mutane ke yi wa waɗanda suka mutu jana’iza, sai bom na uku ya tashi, inda nan ma wata mace ta tayar da shi tare da kashe wasu”, in ji daraktan na SEMA.

Ya ƙara da cewa bom na huɗu ya fashe ne a asibiti, wanda wata matashiya ta tayar a lokacin da jami’an hukumar da likitoci ke taimaka wa waɗanda hare-haren farko suka jikkata.

“Kawo yanzu mutum 18 ne suka suka mutu, da suka haɗa da maza da mata da ƙananan yara da mata masu juna biyu. Mutum 19 da suka samu munanan raunuka an kai su babban asibitin Maiduguri domin basu kulawar gaggawa” in ji Saidu.

Ya kuma ce akwai wasu ƙarin mutum 23 da ke jiran rakiyar sojoji domin kai su asibitin.

Tuni dai sojoji suka sanya dokar hana fita a faɗin ƙaramar hukumar Gwoza, sakamkon hare-haren.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp