fidelitybank

Mutane 18 da Shanu 16 sun mutu a hanyar Legs

Date:

Akalla ‘yan kasuwa 18 ne suka rasu a hatsarin mota kan hanyar su ta kai shanu zuwa Legas daga Sokoto a yammacin ranar Litinin.

A cewar rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ta ce, an kai fasinjoji 42 da suka samu raunuka a hatsarin zuwa asibiti a yankin Gwandu da ke jihar.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, shanu 16 sun mutu a hatsarin.

Kakakin ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar, ya ce hatsarin ya faru ne lokacin da direban wata babbar mota É—auke da fasinjoji da shanu daga yankin Illela na jihar Sokoto ya kauce hanya a mahaÉ—ar Malisa, inda nan take motar ta faÉ—i kasa.

Ya ce hakan ne ya janyo rasuwar fasinjoji 18 yayin da 42 kuma suka samu raunuka daban-daban.

SP Nafiu Abubakar ya kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar ta Kebbi, Ahmed Magaji Kontagora, ya tura jami’an ‘yan sanda zuwa wajen domin É—aukar waÉ—anda suka jikkata zuwa asibiti don yi musu magani.

Kwamishinan ‘yan sandan ya miÆ™a ta’azziya zuwa ga iyalan waÉ—anda suka rasu, inda kuma ya buÆ™aci kungiyoyin NURTW da NARTO da sauran masu amfani da hanya da su rika lura da abubuwan rage gudu da kaucewa É—aukar kaya fiye da Æ™ima da kuma mayar da hankali yayin tuki.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp