Hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) reshen jihar Kaduna, ta ce akalla mutane 16 ne suka mutu sannan wasu 27 suka samu raunuka a wani hatsarin mota da ya rutsa da su a hanyar Kaduna zuwa Abuja.
Kwamandan sashin, Mista Kabir Nadabo, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN cewa mummunan hadarin motan ya afku ne a kauyen Audu Jhangon da ke kan babbar hanyar ranar Lahadi.
Ya bayyana cewa hatsarin ya afku ne da karfe 05:20 na safe, inda wata tirela ta Daf mai lamba KUJ 430XC, dauke da kaya da yawa, ta rasa yadda za ta yi, ta fada cikin rami.
“Rahotanni na farko sun nuna direban na cikin tsananin gudu, watakila saboda gajiya.
“Tawagar masu aikin ceto na RS1.114 Zhipe Unit Command da RS1.16B Dutse Outpost ne suka gudanar da aikin ceton.
“Hatsarin ya rutsa da mutane 65, inda 27 suka jikkata, sannan mutane 16 suka mutu.
“An kai wadanda suka jikkata zuwa asibiti mafi kusa don yi musu magani,” in ji shi.
Nadabo ya ce da samun labarin hatsarin, ya ziyarci wurin ne domin samun bayanai na gani da ido tare da jagorantar tawagar masu aikin ceto wajen kwashe marigayin zuwa dakin ajiye gawa.
“Na kuma umurci motar daukar kaya da ta cire wani bangare na tirelar da ta yi hadari da ta tare wani bangare na hanyar. Ana ci gaba da gudanar da aikin, kuma titin ba shi da walwala don zirga-zirga,” in ji Nadabo (NAN)