fidelitybank

Mutane 16 sun mutu 27 sun jikkata a titin Kaduna zuwa Abuja – FRSC

Date:

Hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) reshen jihar Kaduna, ta ce akalla mutane 16 ne suka mutu sannan wasu 27 suka samu raunuka a wani hatsarin mota da ya rutsa da su a hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Kwamandan sashin, Mista Kabir Nadabo, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN cewa mummunan hadarin motan ya afku ne a kauyen Audu Jhangon da ke kan babbar hanyar ranar Lahadi.

Ya bayyana cewa hatsarin ya afku ne da karfe 05:20 na safe, inda wata tirela ta Daf mai lamba KUJ 430XC, dauke da kaya da yawa, ta rasa yadda za ta yi, ta fada cikin rami.

“Rahotanni na farko sun nuna direban na cikin tsananin gudu, watakila saboda gajiya.

“Tawagar masu aikin ceto na RS1.114 Zhipe Unit Command da RS1.16B Dutse Outpost ne suka gudanar da aikin ceton.

“Hatsarin ya rutsa da mutane 65, inda 27 suka jikkata, sannan mutane 16 suka mutu.

“An kai wadanda suka jikkata zuwa asibiti mafi kusa don yi musu magani,” in ji shi.

Nadabo ya ce da samun labarin hatsarin, ya ziyarci wurin ne domin samun bayanai na gani da ido tare da jagorantar tawagar masu aikin ceto wajen kwashe marigayin zuwa dakin ajiye gawa.

“Na kuma umurci motar daukar kaya da ta cire wani bangare na tirelar da ta yi hadari da ta tare wani bangare na hanyar. Ana ci gaba da gudanar da aikin, kuma titin ba shi da walwala don zirga-zirga,” in ji Nadabo (NAN)

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp