Mutum 13 sun mutu sakmakon wani hatsarin mota a jihar Ondo.
Hatsarin ya afku ne tsakanin wasu motocin bas biyu a daidai wata gada da ake kira Ose da ke kan babban hanyar Owo/Ikare-Akoko.
Ganau sun bayyana cewa haÉ—arin ya faru da misalin karfe 10 na safiyar yau Asabar, inda lamarin ya rutsa da mutum 14.
Mutum 13 daga cikinsu sun ƙone ƙurmus yayin da aka ceto wani guda da ya samu munanan raunuka.
Babban kwamandan hukumar kiyaye haɗura ta jihar Ondo, Samuel Ibitoye, ya tabbatar wa da gidan talbijin na Channels faruwar lamarin, inda ya ce tayan ɗaya daga cikin motocin ne ya fashe abin da ya janyo motar ta ƙwace wa direba har ta kai suka yi karo da wata motar bas, inda nan take suka kama da wuta.
Ya ce jami’ansu sun garzaya zuwa wajen da lamarin ya faru,inda suka mutumin da ya jikkata zuwa asibitin gwamnatin tarayya da ke Owo domin ba shi kulawa.