fidelitybank

Mutane 13 sun kamu da cutar zazzaɓin Dengue a Sokoto

Date:

Hukumar kula da cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya, NCDC ta tabbatar da ɓarkewar cutar zazzabin Dengue a jihar Sokoto.

Babban Daraktan hukumar ta NCDC, Dakta Ifedayo Adetifa wanda ya bayyana haka cikin wata sanarwa da aka fitar a Abuja, ya ce mutum 71 ake zargin sun kamu da cutar, an tabbatar da mutum 13 sun kamu sai dai babu rahoton asarar rai daga ƙananan hukumomin jihar uku da aka samu ɓullar cutar.

Adetifa ya bayyana cewa galibin mutanen da ake zargin sun kamu da cutar ƴan shekara tsakanin 21 da kuma 40 ne inda ya ce an gano hakan cikin watan Nuwambar 2023.

Babban daraktan hukumar ya ce ɓarkewar cutar a yanzu yana mataki na matsakaici la’akari da binciken da aka yi game da haɗarin cutar. Ya kuma ce akwai isassun kayan aiki da kuma ma’aikatan lafiyar da za su duƙufa ko da an samu ɓarkewar cutar a sauran jihohin ƙasar.

Adetifa ya shawarci ƴan Najeriya musamman mazauna jihar Sokoto da su yi riƙo da dukkan matakan kariya kamar sanya kayan da za su rufe jikinsu domin kare kansu daga cizon sauro sannan su kwanta a gidan sauro mai magani.

Sannan a cewarsa, ya kamata mutane su riƙa amfani da maganin sauro a wuraren da suke kwana tare da tabbatar da tsaftar muhallansu domin kare bai wa sauro mafaka.

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp