Mutane goma sha biyu sun mutu a wani haɗarin mota da ya faru a daren da ya gabata na Talata, a kan hanyar Bayamari zuwa Geidam a jihar Yobe da ke arewa maso gabashin Najeriya.
Mutanen sun ƙunshi maza manya goma da babbar mace ɗaya da kuma wata ‘yar ƙaramar yarinya ɗaya, kamar yadda shugaban hukumar kiyaye haɗura ta ƙasar, reshen jihar ta Yobe, Livinus Yilzoom ya bayyana a wata sanarwa ga manema labarai, a babban birnin jihar, Damaturu.
Kwamandan ya ce haɗarin ya faru ne da misalin ƙarfe goma na daren da ya gabata a ƙauyen Chelluri daidai kilomita 20, a kan hanyar Bayamari zuwa Geidam.
Ya ce haɗarin ya afku ne lokacin da motar da mutanen da suka rasu ke ciki, kirar Sharon ta yi karo da wata babbar mota ƙirar Howo ta wani kamfanin aikin gine-gine wadda take tsaye a hanya.
Mista Yilzoom, ya ce karon da Sharon ɗin ta yi ne ta kama da wuta kuma mutanen da ke cikinta suka ƙone yadda ba za a iya gane su ba.