fidelitybank

Mutane 12 sun mutu bayan sun sha Barasa

Date:

Yan sanda a arewa maso yammacin Uganda na bincike a kan mutuwar wasu mutum 12 da ake zargi sun sha wata barasa da aka yi a gida.

Rahotanni sun ce mutanen sun mutu ne a tsakanin ranakun Asabar da Lahadi a lardin Madi-Okollo.

Kazalika an kwantar da wasu da dama a asibiti bayan da suka sha barasar mai suna City 5 Pineapple Flavoured Gin, ciki har da mutumin da yake sayar da ita.

‘Yan sandan sun ce ba a kai ga gano abubuwan da ake hada barasar ba, to amma an bayyana cewa akwai ruwan da aka tace da karin wasu nau’ukan barasar a cikin abubuwan da aka yi amfani da su wajen hada barasar.

Mai magana da yawun rundunar a yankin da lamarin ya afku, ya ce, an karbi samfurin barasar domin gwaji da kuma bincike.

Sannan an kama wasu mutum hudu da ake zargi, kuma an rufe wajen da ake hada barasar.

Mutuwa bayan an sha barasa a Uganda ya zamo ruwan dare gama duniya, inda ko a 2010 sai da mutum 80 suka mutu a kudu maso yammacin kasar bayan sun sha barasa. In ji BBC.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp