fidelitybank

Mutane 12 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Nasarawa

Date:

Majalisar dokokin jihar Nasarawa ta ce, mutane 12 ne suka mutu a wani hatsarin kwale-kwale a kogin Kogi, Kungra Kamfani, a unguwar Arikiya da ke karamar hukumar Lafia a ranar 20 ga watan Agusta.

Alhaji Ibrahim Abdullahi, shugaban majalisar ne ya bayyana haka a wani taron gaggawa da majalisar ta gudanar a ranar Alhamis a garin Lafiya.

Abdullahi ya jajantawa kananan hukumomin jihar da na Lafia bisa afkuwar lamarin.

Ya kuma jajantawa iyalan wadanda suka rasu bisa rasuwar ‘yan uwansu.

“Abin bakin ciki ne matuka yadda muka rasa mutane 12 da suka hada da maza da mata a wani hatsarin jirgin ruwa a Arikiya da ke karamar hukumar Lafia.

“Mutane 19 ne ke cikin jirgin, 12 sun mutu sannan bakwai aka ceto. An jefa karamar hukumar Lafiya da jiharmu cikin alhini kan wannan lamari mai ban tausayi,” inji shi.

Majalisar wadda ta bayyana lamarin a matsayin abin takaici, sai dai ta bukaci ‘yan uwa da al’ummar karamar hukumar Lafia da gwamnatin jihar da su dauki wannan rashi da ba za a iya kwatantawa ba.

“A madadina, Honourable members da kuma ma’aikata, muna jajantawa iyalan mamatan, karamar hukumar Lafia da gwamnatin jihar bisa rasuwarsu.

“Muna addu’ar Allah ya hutar da rayukansu,” in ji kakakin.

Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta wa wadanda abin ya shafa kurakuransu, ya kuma sa su huta.

Daga baya ‘yan majalisar sun yi shiru na minti daya domin girmama rayukan da suka rasu.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp