fidelitybank

Mutane 12 ne suka ƙone ƙurmus a Rivers – Ƴa Sanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Rivers ta tabbatar da cewa, mutane 12 ne suka mutu sakamakon fashewar wani abu da ya faru da safiyar Juma’a a kauyen Rumuekpe da ke karamar hukumar Emoha a jihar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Grace Iringe-Koko, ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal, inda ta ce binciken farko ya nuna cewa wadanda abin ya shafa na diban danyen man ne lokacin da wurin ya kama wuta.

Fashewar ta afku a daidai lokacin da wata motar bas dauke da danyen mai ta kama da wuta, a lokacin da take barin wurin zuwa wata matatar mai ta haramtacciyar hanya a yankin.

“Ya zuwa yanzu kimanin mutane 12 ana kyautata zaton sun kone kurmus. Har yanzu ba a san ko su waye wadanda abin ya shafa ba,” inji ta.

Iringe-Koko ya kuma ce an kona motoci biyar da babura uku hudu a wurin fashewar.

A halin da ake ciki, rundunar ‘yan sandan ta gargadi jama’a da su nisanta kansu daga hada-hadar man fetur ba bisa ka’ida ba, su tuntubi ta lambobin waya, 08032003514 da 08098880134, domin kai rahoton duk wani laifi.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp