Mutum 11 sun ƙone ƙurmus a mummunan haɗarin mota da ya ritsa da ababe hawa daban-daban a yankin Ochadamu na Jihar Kogi.
Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC), ta faɗa cikin wata sanarwa ranar Alhamis cewa hatsarin ya ritsa da ababen hawa 20.
Jami’in hulɗa da jama’a na FRSC, Bisi Kazeem, ya ce za a iya kare afkuwar haɗurran, yana mai kira ga masu ababen hawa da su dinga kula da abin hawan nasu akai-akai.
“Tawagar bincike ta ba da rahoton cewa lamarin ya ritsa da mutum 18,” in ji shi.
“Daga cikinsu, mutum bakwai – uku maza huɗu mata sun ji raunuka daban-daban, yayin da sauran 11 ɗin waɗanda ba a iya tantance jinsinsu ba ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton suka ƙone ƙurmus.”
Ya ƙara da cewa rahoton ya bayyana dalilin faruwar hatsarin da lalacewar titi, da shanyewar birki, da rashin ingancin abin hawa.