fidelitybank

Mutane 10 sun mutu a wani hatsari da ya auku a jihar Jigawa

Date:

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutum 10 a wani hatsarin mota a ƙauyen Yanfari da ke karamar hukumar Taura na jihar.

Lamarin wanda ya afku a yau Talata, 12 ga watan Nuwamba a daidai hanyar Kano-Hadejia, ya kuma janyo jikkatar wani fasinja ɗaya.

Wata sanarwa da kakakin ƴansandan jihar DSP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, ya ce lamarin ya afku ne lokacin da wata motar ƙirar bas da ta fito daga jihar Kano zuwa Hadejia ɗauke fa fasinjoji 11, ta garu da wata tirela har ta kai suka jujjuya.

“Nan take direban motar tare da wasu fasinjoji tara da ya ɗauka suka mutu,” in ji sanarwar.

Bayan afkuwar lamarin, tawagar sintiri na ƴansandan reshen Taura suka garzaya wajen, inda suka ɗauki gawawwakin waɗanda suka mutu zuwa babban asibitin Hadejia.

Sun kuma ce sauran fasinja guda da ya jikkata na samun kulawa a cibiyar kiwon lafiya na Majia.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp