Harin makamai masu linzami da Hezbollah ta harba daga Lebanon zuwa biranen Haifa da Tiberian na arewacin Isra’ila a cikin dare ya jikkata mutum goma, kamar yadda hukumar ko ta kwana ta Isra’ila.
Hukumar ta ce yawancin waÉ—anda suka jikkata, sun samu raunuka ne a sanadiyar fashewar gilasai da tagogi da sauran abubuwa.
Makamai masu linzamin sun sauka ne a gidaje da wani wajen cin abinci, kamar yadda rundunar sojin Isra’ila ta bayyana, inda ta Æ™ara da cewa za ta Æ™addamar da bincike domin gano yadda hare-haren makaman suka kauce wa tsaron Æ™asar ba tare an kakkaÉ“o su ba.
Ita dai Hezbollah ta ce ta Æ™addamar da harin ne da niyyar tarwatsa makaman Isra’ila.