Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam’iyyar Labour a zaɓen 2023, Peter Obi, ya yi kira ga Musulmin Najeriya da su ci gaba da jajircewa da kuma yin sadaukarwa.
Mista Obi ya bayana haka ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a don taya al’ummar Musulmi murnar bikin babban sallah.
Ya ce irin wannan lokaci na murnar bikin sallah, tunatarwa ce na ƙarfin imani, yin ladabi da kuma kaskantar d akai.
Tsohon gwamnan na jihar Anambra ya yi fatan cewa murnar bikin wata dama ce ga shugabannin Najeriya a dukkan mataki, na su yi duba kan ɗabi’un kyakkyawan shugabanci.
“Ina taya illahirin al’ummar Musulmi murnar bikin sallah. Ina fatan wannan lokaci zai ƙara ƙarfafa mana haɗin-kai da kuma zaburar da mu wajen aiki don samar da Najeriya mai nagarta. Eid Mubarak,” kamar yadda Mista Obi ya bayyana.