Gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom ya bukaci musulmai da su cigaba da yi wa ƙasa addu’a a matsayin maganin matsalolin tsaro da ke addabar kasar.
Ortom a cikin sakon fatan alheri ga Musulmai a bikin Eid Malud, ya bukaci mabiya addinin Islama da su yi koyi da kyawawan dabi’u na ruhi da Manzon Allah Muhammad ya yi misali da su.
Gwamnan ya zayyana yadda za a yi hadin gwiwa tsakanin kungiyoyin addinai daban-daban da cewa hakan zai tabbatar da zaman lafiya, tsaro da zaman lafiya a kasar nan.
Ya kuma umarci al’ummar Musulmi da su sadaukar da lokacin bikin domin yi wa Nijeriya addu’ar zaman lafiya da hadin kan kasa musamman ganin yadda zaben 2023 ke gabatowa.
Gwamna Ortom ya bayar da shawarar cewa ya kamata dukkan ‘yan Najeriya su shiga harkar samar da zaman lafiya domin a samu kasar ta yi aiki don amfanin ‘yan kasa.
Ya yi wa ‘yan Nijeriya fatan a yi bukukuwan lafiya da kwanciyar hankali.
Ana gudanar da Idi -Malud duk shekara domin tunawa da haihuwar Annabi Muhammadu SAW.