Jami’an tsaro a Addis Ababa, babban birnin Ethiopia, sun fesa barkokon-tsohuwa kan wasu Musulmai da suka taru domin gudanar da sallar Idi.
Dubban Musulmai ne suka taru a babban filin wasan birnin inda kuma a nan ake sallar Idi amma rikici ya barke. Ba a samu rahoton mutuwa ba.
Lamarin ya faru ne kwanaki kadan bayan da aka tayar da jijiyoyin wuya tsakanin Musulmai da Kiristoci a sassan kasar bayan an kashe Musulmai 20 da ke halartar jana’iza a makon jiya a arewacin Ethiopia.
Bayan aukuwar lamarin a birnin Gondar, an gudanar da jerin zanga-zanga a wurare da dama da kuma tarzoma ciki har da kona akalla coci uku a kudancin kasar.
Matakin da jami’an tsaro suka dauka na fesa barkonon-tsohuwa kan Musulman zai iya dagula lamura.
An ga hotunan mutane suna tserewa yayin da ake wurga musu barkonon-tsohuwa da kuma mata da ke neman ‘ya’yansu cikin kaduwa.
Rundunar ‘yan sandan Addis Ababa ta dora alhakin lamarin kan “wasu tsirarun mutane” kuma ta ce an lalata wurare da dama. A cewar BBC.