Wasu ‘yan Acaba da ‘yan sanda a jihar Oyo, sun tabbatar da cewa, su ne suke siyo wa masu garkuwa da mutane abinci da abin sha.
Daya daga cikin ‘yan acaban da ya shiga hannu, ya bayyana cewa a na biyansu Naira 10,000 a duk lokacin da suka karbi sakon na masu garkuwar.
Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Oyo, Ngozi Onadeko, yayin holin wadanda ake zargin ta ce, rundunar ta samu nasarori sosai, saboda tattara bayanan sirri.
Wasu gungun mutane sun amsa cewa suna da hannu cikin sace mutane da aka yi a baya-bayan nan a babban titin Legas zuwa Ibadan wacce ta yi sanadin mutuwar wani mutum mai shekara 45, Oluwatosin Anwajoye.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa, wadanda ake zargin sun tabbatar da cewa, suna da hannu a satar mutane da aka yi a ranar 7 ga watan Janairun 2022 a Onigara, babban titin Legas zuwa Ibadan.