Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya ce a yanzu sojoji da manyan kwamandojin na “Zirin Gaza, kuma an baza su ko’ina a yankin”.
Tun da farko shugaban Turkiya, Recep Tayyip Erdogan, ya zargi Isra’ila da aikata laifukan yaƙi.
Firaministan na Isra’ila bai kama sunan Erdogan ba, amma ya ce “Kada ka zargemu da aikata alifukan yaƙi, idan kana tunanin za ka zargi sojojinmu da aikata laifukan yaƙi wannan munafurci ne, Mu ne ke da sojoji mafiya tsafta a duniya.”
Ya ce rundunar sojin ƙasar na ɗaukar matakan da suka dace wajen kare fararen hula, tare da zargin Hamas da aikata laifukan ci zarafi ta hanyar “amfani da mutane a matsayin garkuwa”.
Ma’aikatar lafiya a Gaza da ke ƙarƙashin ikon Hamas, ta ce fiye da mutum 7,600 aka kashe a Gaza tun bayan da Isra’ila ta fara kare hare-haren bom a yankin.
A ranar Juma’a Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, ta ce kashi 40 na wadanda ka kashe ƙananan yara ne.
Hamas ta kashe fiye da mutum 1,400 a hare-haren da ta kai Isra’ila ranar 7 ga watan Oktoba, mafiya yawansu fararen hula, ciki har da mata da ƙananan yara.