fidelitybank

Muna ƙoƙarin kuɓutar da Sarkin Gurku da iyalinsa – ‘Yan Sanda

Date:

Rundunar ƴan sanda a jihar Nasarawar ta ce, jami’anta na can suna ƙoƙarin kuɓutar da mai martaba Sarkin Gurku da iyalinsa, waɗanda ƴan bindiga suka sace.

Rundunar `yan sandan ta tabbatar da cewa da misalin karfe goma na dare, maharan waɗanda ake zargin masu satar mutane ne ɗauke da bindigogi suka kutsa fadar mai martaba Sarkin Gurku, mai daraja ta ɗaya, Alhaji Jibrin Mohammed, bayan sun kaikaici lokacin da aka watse daga fada, wadda ke da tazarar kilomita goma da marabar Gurku da ke jikin babbar hanyar da ta tashi daga Abuja ta dangana da Keffi, inda suka tafi da shi da mai ɗakinsa.

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar ta Nasarawa, Rahman Nansel, ya ce an yi wa rundunar `yan sanda kiran neman ɗauki a ranar 6 ga watan Agusta, cewa wasu da ake zargin masu satar mutane ne sun kai samame fadar mai martaba sarkin Gurku.

Nan da nan kwamishinan `yan sanda ya tura jami’ansa zuwa fadar tare da haɗin-gwiwa da ƴan banga.

Suna isa suka tarar an sace sarkin da iyalinsa, kuma ba a san inda aka tafi da su ba. An karaɗe dazukan da ke kewaye amma ba a yi nasarar samun su ba.“

Kakakin ƴan sandan ya ce jami`ansu sun bazama, suna ƙoƙarin gano maɓoyar ‘yan bindigan don ceto basaraken da mai ɗakin nasa.

Jihar Nasarawa na maƙwabtaka da jihohi da dama da ke fama da ƙalubalen da ya shafi tsaro, ciki har da Binuwai da Plateau da Kaduna da Kogi da kuma Abuja, babban birnin tarayya.

Ko a watan jiya, gwamnan jihar Abdullahi Sule ya nuna damuwa game da yadda miyagun da aka fatattaka a jihohi makwabta ke kwarara jiharsa. Har ma ya buƙaci hedikwatar tsaron Najeriya da ta taimaka wajen dakile miyagun.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp