fidelitybank

Muna tir da kisan mutane 37 a Borno – MDD

Date:

Majalisar Dinkin Duniya ta yi Alla-wadai da kisan fararen hula akalla 37 a wani harin kwantan ɓauna a ƙauyen Mukdolo a karamar hukumar Ngala na jihar Borno.

Rahotanni sun ce gwamman mutane ne waɗanda akasari manoma da masunta aka harbe a harin da ake zargin mayaƙan ISWAP da kai wa.

Harin ya faru ne a garin Dikwa wanda ke kusa da garuruwan da ‘yan ta-da-ƙayar-baya na Boko Haram ke da karfi.

Karanta Wannan: Ba za mu amince da harin da ake kaiwa kabilar mu ba – Kungiyar Inyamurai

Mutane da dama ne suka jikkata a harin yayin da wasu da yawa kuma suka ɓata. An kashe manoman ne a ranar Laraba lokacin da suka je daji neman itace.

Majiyoyin tsaro sun ce gwamman mayaƙan na ISWAP sun yi wa garin dirar miƙiya a kan babura, inda bayan isarsu suka fara harbi kan mai uwa da wabi. Mutum tara ne kuma suka samu damar tserewa.

A cikin wata sanarwar da ofishin kodinetan ba da agaji na MDD Mista Mathias Schmale ya fitar, ya mika ta’aziyya ga iyalan da suka rasa ‘yan uwansu.

Ya ce akasarin waɗanda lamarin ya rutsa da su masunta ne da manoma waɗanda ke neman samun abin da dogaro da rayuwarsu.

“Wannan harin abin tayar da hankali ne kuma hakan ya sake nuna barazana da halin rashin tsaro da ‘yan gudun hijira da sauran mutanen da ayyukan ‘yan ta-da-ƙayar-baya na shekara sama da 13 ay shafa ke ciki a yankin. Mutane sun tserewa ƙauyen Mukdolo kafin kawo wannan hari sanadiyyar ayyukan kungiyoyi masu ikirarin jihadi,” in ji sanarwar.

Mista Schmale ya yi kira ga hukumomin jihar da suka gaggauta gudanar da bincike kan lamarin da nufin hukunta waɗanda aka samu da laifi.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp