fidelitybank

Muna tir da kisan mutane 37 a Borno – MDD

Date:

Majalisar Dinkin Duniya ta yi Alla-wadai da kisan fararen hula akalla 37 a wani harin kwantan ɓauna a ƙauyen Mukdolo a karamar hukumar Ngala na jihar Borno.

Rahotanni sun ce gwamman mutane ne waɗanda akasari manoma da masunta aka harbe a harin da ake zargin mayaƙan ISWAP da kai wa.

Harin ya faru ne a garin Dikwa wanda ke kusa da garuruwan da ‘yan ta-da-ƙayar-baya na Boko Haram ke da karfi.

Karanta Wannan: Ba za mu amince da harin da ake kaiwa kabilar mu ba – Kungiyar Inyamurai

Mutane da dama ne suka jikkata a harin yayin da wasu da yawa kuma suka ɓata. An kashe manoman ne a ranar Laraba lokacin da suka je daji neman itace.

Majiyoyin tsaro sun ce gwamman mayaƙan na ISWAP sun yi wa garin dirar miƙiya a kan babura, inda bayan isarsu suka fara harbi kan mai uwa da wabi. Mutum tara ne kuma suka samu damar tserewa.

A cikin wata sanarwar da ofishin kodinetan ba da agaji na MDD Mista Mathias Schmale ya fitar, ya mika ta’aziyya ga iyalan da suka rasa ‘yan uwansu.

Ya ce akasarin waɗanda lamarin ya rutsa da su masunta ne da manoma waɗanda ke neman samun abin da dogaro da rayuwarsu.

“Wannan harin abin tayar da hankali ne kuma hakan ya sake nuna barazana da halin rashin tsaro da ‘yan gudun hijira da sauran mutanen da ayyukan ‘yan ta-da-ƙayar-baya na shekara sama da 13 ay shafa ke ciki a yankin. Mutane sun tserewa ƙauyen Mukdolo kafin kawo wannan hari sanadiyyar ayyukan kungiyoyi masu ikirarin jihadi,” in ji sanarwar.

Mista Schmale ya yi kira ga hukumomin jihar da suka gaggauta gudanar da bincike kan lamarin da nufin hukunta waɗanda aka samu da laifi.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp