fidelitybank

Muna tir da harin da aka kai ofishin SDP – Gwamnatin Kogi

Date:

A ranar Lahadin da ta gabata ne gwamnatin jihar Kogi, ta yi Allah wadai da lalata kadarori na jam’iyyar Social Democratic Party, SDP, ofishin yakin neman zaben da ke Lokoja.

DAILY POST ta ruwaito cewa wasu da ake zargin ‘yan daba ne da sanyin safiyar Lahadi, suka mamaye ofishin yakin neman zaben jam’iyyar SDP da ke kusa da kasuwar Paparanda Kpata, inda suka lalata allunan tallace-tallacen da ke nuna hoton shugaban kasa Bola Tinubu tare da dan takarar Gwamnan Jihar Kogi na SDP a ranar 11 ga watan Nuwamba. Alhaji Murtala Yakubu Ajaka.

Da yake mayar da martani kan lamarin ta wata sanarwa da ya fitar a yammacin ranar Lahadi, kwamishinan yada labarai da sadarwa, Kingsley Fanwo, ya bayyana lamarin a matsayin dabbanci, rashin bin tafarkin dimokaradiyya da kuma rashin amincewa da jama’a da gwamnatin jihar.

Ya ce gwamnatin jihar za ta ci gaba da tallafawa ’yancin kowa da kowa don neman mukamai daidai da ka’idojin demokradiyya.

Fanwo ya ce, “Har wa ofishin yakin neman zaben kowace jam’iyyar siyasa laifi ne kuma ba za a amince da shi ba.”

Kwamishinan ya yi kira ga hukumomin tsaro a jihar da su gudanar da bincike tare da kama wadanda suka kai harin domin gurfanar da su a gaban kuliya tare da gargadin ‘yan daba cewa zaben gwamna a jihar za a yi shi ne da kuri’a ba ta hanyar harsashi ba.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp