China ta yi Allah-wadai da matakin Sweden na ƙona al-Kur’ani.
“‘Yancin fadin albarkacin baki ba hujja ba ne ba cin zarafi ko nuna wariya, wanda ke raba kan al’umma,” in ji Wang Wenbin, kakakin ma’aikatar harkokin wajen China.
“Muna fatan Sweden za su mutunta musulmai marasa rinjaye da addininsu,” kamar yadda ya bayyanawa jaridar Global Times.
A watan jiya ne, Rasmus shugaban masu tsattsauran ra’ayi ya kona Kur’ani a Linkoping, da ke Sweden. Kuma ya yi barazanar zai kona wasu littatafai na daban.