Wasu da ba a san ko su waye ba sun kona ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC da ke karamar hukumar Orlu a jihar Imo.
Masu kone-kone sun kai hari a ginin da ake yi wa kwaskwarima a ranar Alhamis.
Kwamishiniyar zabe ta INEC reshen jihar Imo, Farfesa Sylvia Agu, ta tabbatar da harin a cikin wata sanarwa da kwamishiniyar yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a Festus Okoye ta fitar a jiya, kamar yadda NAN ta ruwaito.
“Al’amarin ya faru ne a ranar Alhamis, 1 ga Disamba, 2022.
“Gini, wanda ake yin gyare-gyare sosai bayan harin da aka kai a baya, an lalata shi kuma an kone shi a wani bangare,” in ji shi.
Okoye ya ce, an yi garkuwa da wasu daga cikin wadanda ke aiki a wurin amma daga baya aka sake su.
Ya bayyana cewa, shiga tsakani da ‘yan sandan da aka tura wurin suka yi a kan lokaci ya rage barnar da aka samu.
“Da ma barnar ta fi yawa amma ga gaggawar da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta bayar wanda ta tura jami’anta zuwa wurin.
“Wannan hari daya ne ya yi yawa,” in ji shi.
INEC ta nuna damuwarta kan hare-haren da aka kai kan cibiyoyinta a fadin kasar nan gabanin babban zabe na 2023.
Hukumar ta lura cewa irin wadannan hare-haren suna da mummunan sakamako kan shirye-shiryenta na 2023.