fidelitybank

Muna takaicin hare-haren da ake kai wa ofisoshin mu – INEC

Date:

Wasu da ba a san ko su waye ba sun kona ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC da ke karamar hukumar Orlu a jihar Imo.

Masu kone-kone sun kai hari a ginin da ake yi wa kwaskwarima a ranar Alhamis.

Kwamishiniyar zabe ta INEC reshen jihar Imo, Farfesa Sylvia Agu, ta tabbatar da harin a cikin wata sanarwa da kwamishiniyar yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a Festus Okoye ta fitar a jiya, kamar yadda NAN ta ruwaito.

“Al’amarin ya faru ne a ranar Alhamis, 1 ga Disamba, 2022.

“Gini, wanda ake yin gyare-gyare sosai bayan harin da aka kai a baya, an lalata shi kuma an kone shi a wani bangare,” in ji shi.

Okoye ya ce, an yi garkuwa da wasu daga cikin wadanda ke aiki a wurin amma daga baya aka sake su.

Ya bayyana cewa, shiga tsakani da ‘yan sandan da aka tura wurin suka yi a kan lokaci ya rage barnar da aka samu.

“Da ma barnar ta fi yawa amma ga gaggawar da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta bayar wanda ta tura jami’anta zuwa wurin.

“Wannan hari daya ne ya yi yawa,” in ji shi.

INEC ta nuna damuwarta kan hare-haren da aka kai kan cibiyoyinta a fadin kasar nan gabanin babban zabe na 2023.

Hukumar ta lura cewa irin wadannan hare-haren suna da mummunan sakamako kan shirye-shiryenta na 2023.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Æ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Æ™asa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp