fidelitybank

Muna takaicin hare-haren da ake kai wa ofisoshin mu – INEC

Date:

Wasu da ba a san ko su waye ba sun kona ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC da ke karamar hukumar Orlu a jihar Imo.

Masu kone-kone sun kai hari a ginin da ake yi wa kwaskwarima a ranar Alhamis.

Kwamishiniyar zabe ta INEC reshen jihar Imo, Farfesa Sylvia Agu, ta tabbatar da harin a cikin wata sanarwa da kwamishiniyar yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a Festus Okoye ta fitar a jiya, kamar yadda NAN ta ruwaito.

“Al’amarin ya faru ne a ranar Alhamis, 1 ga Disamba, 2022.

“Gini, wanda ake yin gyare-gyare sosai bayan harin da aka kai a baya, an lalata shi kuma an kone shi a wani bangare,” in ji shi.

Okoye ya ce, an yi garkuwa da wasu daga cikin wadanda ke aiki a wurin amma daga baya aka sake su.

Ya bayyana cewa, shiga tsakani da ‘yan sandan da aka tura wurin suka yi a kan lokaci ya rage barnar da aka samu.

“Da ma barnar ta fi yawa amma ga gaggawar da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta bayar wanda ta tura jami’anta zuwa wurin.

“Wannan hari daya ne ya yi yawa,” in ji shi.

INEC ta nuna damuwarta kan hare-haren da aka kai kan cibiyoyinta a fadin kasar nan gabanin babban zabe na 2023.

Hukumar ta lura cewa irin wadannan hare-haren suna da mummunan sakamako kan shirye-shiryenta na 2023.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan Æ´ansanda mai kula da sashen kai É—auki na...

INEC za ta bai wa É—aurarru damar kaÉ—a Æ™uri’a a lokacin zaÉ“uka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

ÆŠaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon É—an takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaÉ—i mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaÉ—i...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp