Hukumar yaƙi da cin hanci (EFCC), ta bayyana cewa tana neman tsohon ministan makamashi da ƙarafa na kasar, Olu Agunloye, ruwa a jallo.
EFCC na zargin sa ne da almundahanar dala biliyan shida na kwangilar wutar lantarki da aka bayar tun a gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo daga 1999 zuwa 2003.
Rahotonni sun ce kwangilar ta shafi aikin tashar wuta ta Mambila da ke Gembu a jihar Taraba, wadda wani bincike da BBC ya ce, shekara 40 da fara maganarsa.
Tun da farko hukumar ta taɓa gayyatar Mista Agunloye a 2016, inda ta yi masa tambayoyi, sai dai ya sha musanta zarge-zargen.