fidelitybank

Muna neman Sojoji su kawo man dauki rumbun adana abinci – NEMA

Date:

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta bukaci tallafin sojoji domin dakile duk wani abu da ya shafi tsaro a rumbunan abincin ta dake Kaduna.

Kodinetan NEMA na shiyyar arewa maso yamma, Imam Garki ne ya yi wannan kira a lokacin da ya ziyarci kwamandan runduna ta biyu ta sojojin Najeriya, ranar Talata a Kaduna.

Ya ce sun kai ziyarar ne domin karfafa tsaro a rumfunan ajiya daban-daban, biyo bayan aukuwar lamarin da wasu ‘yan daba suka kai hari a cibiyoyin gwamnati domin kwashe kayan abinci da sauran kayayyaki masu daraja.

“Muna nan ne don neman tallafin sojoji don samun matsayin jami’an tsaro na jiran aiki don kiyaye wuraren ajiyar kayayyakin hukumar,” in ji shi.

Ko’odinetan wanda ya samu wakilcin shugaban sashen bincike da ceto na hukumar Abdulkadir Mohammed ya jaddada cewa hukumar na da alaka da rundunar sojojin Najeriya, wanda ke aiki a matsayin daya daga cikin sassan da ke ba da agajin gaggawa (DRUs) na hukumar. .

Da yake mayar da martani, Lt.-Col. Abdulqadir Abdullahi, Kwamandan Bataliya ta 2 na Sojojin Najeriya, ya tabbatar wa hukumar hadin gwiwa da rundunar ta Sojoji wajen shawo kan lamarin.

Babban Darakta, Mista Mustapha Ahmed, ya umurci Daraktocin shiyya da shugabannin ayyuka da su karfafa tsaro a ofisoshin NEMA da ma’aikatun NEMA da kewaye a fadin kasar nan.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp