Jami’an sojin ƙasa da aikin wanzar da zaman lafiya a Jihar Filato ya rataya a wuyansu, sun bayyana cewa, suna samun nasara a yaƙi da ‘yan bindiga kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Da yake magana da jaridar Punch a birnin Jos ranar Litinin biyo bayan kashe ‘yan bindiga takwas da jami’ai suka yi a wani aiki na musamman da ƙaramar hukumar Wase ranar Lahadi, kakakin aikin Manjo Ishaku Takwa, ya ce a ba za a lamunce da ƴan bindiga su cigaba da bin jama’ar gari suna korarsu daga gidajensu a duk wani yanki na jihar ba.
Ya bayyana cewa, ayyukan ƴan bindigar sun yi ɓarna mai yawa a jihar, musamman a yankunan karkara.
A cewar shi, ayyukan korar ƴan bindigan wanda aka fara Asabar din da ta gabata, za a cigaba da shi har sai an yi nasara baki daya akan mayakan.