fidelitybank

Muna maraba da haɗakar Atiku – NNPP

Date:

Jam’iyyar adawa ta NNPP a Najeriya ta nuna aniyarta ta shiga jam’iyyar haɗaka da sauran jam’iyyun adawa kamar yadda Atiku Abubakar ya nema a makon da ya gabata.

Ɗan takarar na jam’iyyar PDP a zaɓen shugaban Najeriya na 2023, Atiku ya zargi APC da yunƙurin mayar da Najeriya bin tsarin jam’iyya ɗaya sannan ya yi kira ga jam’iyyun adawa da su dunƙule don yin waje da jam’iyyar mai mulki.

Shugaban riƙo na NNPP na ƙasa, Abba Kawu Ali, ya bayyana hakan, yayin wani taron manema labarai cewa kiran na Atiku abin a yaba ne.

“NNPP na kallon wannan kira na Atiku a matsayin na kishin ƙasa kuma abin maraba,” in ji shi. Sai dai ya ce suna so a yi wa shirin kwaskwarima.

“Sai dai kuma NNPP na son a sauya wa shirin fuska. Muna ganin ya kamata abin ya ƙunshi kowa da kowa, kuma a faɗaɗa shi. Irin wannan haɗakar jam’iyyu suka yi a 2015 wadda ta ba su damar kayar da jam’iyya mai mulki ta PDP a lokacin.

“Saboda haka muna ganin kiran da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubkar ya yi abin yabawa ne.”

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...
X whatsapp