Kamfanin sayar da wutar lantarki a Najeriya na Kano Electricity Distribution Company (KEDCO), ya sanar da kwastomominsa cewa, za su kasance cikin duhu na tsawon awa takwas a ranar Asabar sakamakon gyaran da yake yi a wata tasharsa da ke jihar Kano.
Kamfanin na KEDCO dai shi ne ke bai wa jihohin Kano da Katsina da Jigawa lantarki, duka a arewacin Najeriya.
A cewar sanarwar da ya aike wa abokan hulÉ—ar tasa, an É—auki matakin ne saboda aikin gyara É—aya daga cikin na’urorin rarraba wutar da ke Kumbotso a cikin birnin Kano.
Za a yi aikin ne daga ƙarfe 10:00 na safe zuwa 6:30 na yamma, a cewar KEDCO.
‘Yan Najeriya na fama da É—aukewar wutar lantarki a dukkan sassan Æ™asar a baya-bayan nan sakamakon lalacewa da babban layin lantarkin ke yawan yi.
Ranar Laraba ma sai da layin ya lalace da misalin ƙarfe 11:27 na rana.