fidelitybank

Muna kokarin sasanta Wike da Atiku – Sanata Ben Obi

Date:

Sanata Ben Obi da Farfesa Obiora Okonkwo, shugaban da Darakta Janar na kungiyar yakin neman zaben Atiku da Okowa a jihar Anambra, sun bayyana cewa wata tawaga ta musamman na kokarin sasanta rikicin da ke tsakanin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar da gwamnonin G5.

Sun bayyana hakan ne a ranar Laraba a garin Awka na jihar Anambra, yayin wani taron manema labarai na tunkarar yakin neman zabe domin sanar da ziyarar Alhaji Atiku Abubakar a ranar Alhamis.

Majalisar kamfen din ta kuma yi amfani da damar wajen gabatar da shirinta na tunkarar dan takarar a jihar Anambra.

Sanata Ben Obi da Okonkwo da suka yi wa manema labarai jawabi sun ce ana ci gaba da kokarin sasanta Atiku da Gwamnonin G5, kuma jihar ta shirya tsaf don baiwa Atiku nasara a zaben 2023.

Obi ya ce: “Abu ne na kowa ga jam’iyyun siyasa su yi rikici. Hakan bai wuce inda ake ba, kuma muna da wata tawaga da ke kokarin ganin an warware rikicin da ke faruwa a PDP.

“Wannan ba abu ne da muke son bayyanawa jama’a ba, amma bari in gaya muku cewa gwamnonin G5 ma suna son a samu zaman lafiya, Wike (Gwamnan Jihar Ribas) ya fadi haka. Muna da tawaga da ke aiki a kan hakan, kuma a yanzu, ba mu son bayyana sakamakon ga jama’a, amma muna aiki.”

Okonkwo ya kuma kara da cewa: “Ko a jihohin da ake fama da wannan rikici, har yanzu ana ci gaba da yakin neman zabe, kuma shirin shi ne zaben PDP daga sama har kasa. A Abia kun ji taken sama da biyar, kuma duk gwamnoninmu suna ta yakin neman zaben Atiku.

“A dukkan bukatun su (G5) ba su taba cewa suna da wata matsala da Atiku da kan su ba. Ba al’amari ne da ba za a iya warware shi ba.”

Da yake magana a kan shirin dan takarar a Anambra a ranar Alhamis, Okonkwo ya ce jam’iyyar na sa ran za a gudanar da gagarumin gangami, kuma an shirya masa ayyuka da dama.

“Zuwa da karfe 10 na safe, za mu hadu da shi a filin jirgin sama sannan mu wuce zuwa masaukin Gwamna, inda dan takarar shugaban kasa zai gana da Gwamna Chukwuma Soludo. Daga nan ne zai yi wata ganawa ta bangaranci da sarakunan gargajiya na jihar Anambra.

“Zai kaddamar da ofishin yakin neman zabe, sannan kuma zai yi mu’amala da shugabannin kungiyar, shugabannin kasuwa, a cibiyar Ekwunife, kafin kaddamar da yakin neman zabe.”

A baya dai jam’iyyar ta bada sanarwar hutu a tsakanin daukacin ‘ya’yan jam’iyyar PDP na jihar, kuma Okonkwo ya ce matakin ya tsaya, kuma ana sa ran samun dimbin jama’a a yakin neman zaben.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko Ĉ´anĈ™wallon...

Sunderland ta ɗauko Ĉ´anĈ™wallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan Ĉ™wallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ĉ˜ungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ĉ˜ungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp