Shugaban jam’iyyar APC reshen jihar Filato, Rufus Bature, ya ce, jam’iyyar a shirye take ta fara yunkurin sulhuntawa a kananan hukumomi 17 na jihar.
Bature ya bayyana haka ne ga manema labarai jiya a sakatariyar jam’iyyar APC da ke Jos jim kadan bayan kaddamar da shugabannin zartaswar jam’iyyar na jihar.
Ya bayyana cewa, jam’iyyar na tsara hanyoyin da za ta iya karbar sabbin mambobinta, inda ya ce, akwai jiga-jigan da ke shirin komawa APC.
Ya ce: “Wannan ita ce rantsuwar ‘yan majalisar zartaswar jihar. Na yi rantsuwa da kaina a Abuja, domin haka ina bukatar in zo in kaddamar da Exco members dina.