fidelitybank

Muna jajanta wa mawaki Davido mutuwar dan sa Ifeanyi – Keyamo

Date:

Kakakin kungiyar yakin neman zaben Tinubu/Shettima, Festus Keyamo, ya jajanta wa mawaki David Adeleke da amaryarsa Chioma Rowland bisa rasuwar dansu, Ifeanyi.

Rahotanni sun ce Ifeanyi ya nutse a ranar Litinin a gidan mawakin na Banana Island.

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas, wadda ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Talata, ta kuma ce an kawo ma’aikatan gida takwas domin yi musu tambayoyi kan lamarin.

Da yake mayar da martani, Keyamo ya jajantawa iyalan.

Ya rubuta, “A gaskiya ina jiran bayanin iyali kan wannan don in tabbata. Ta’aziyyata ga wannan matashin iyali da suka fuskanci wannan bakin ciki a wannan lokaci.

“Allah Madaukakin Sarki Ya ba iyalan Adeleke kwarin guiwar jure wannan rashin da ba za a iya maye gurbinsa ba; da kuma duk wadanda suka sha irin wannan rabo”.

Shima da yake mayar da martani, mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmed ya yi addu’ar Allah ya jikan ma’auratan.

“Tunanina da addu’a na tare da @Davido, wanda ya yi rashin dansa, Ifeanyi. Babu wani iyaye da ya isa ya fuskanci rasa ɗa a cikin irin wannan mummunan lamari.

“Allah ya jikan shi da Chioma, uwar yaron.”

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp