Sanatocin jam’iyyar APC da ke zama a zauren majalisar dokokin kasar nan sun sake dagewa kan rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar APC cewa, Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe ya maye gurbin Gwamnan Jihar Neja, Sani Bello. a matsayin Shugaban riko na jam’iyyar.
Bayan shafe kwana biyu suna gudanar da taron gaggawar sun bayyana cewa, Buni ya ci gaba da zama shugaban kwamitin riko/tsare na musamman na jam’iyyar.
Da yake gabatar da tambayoyi daga manema labarai bayan ganawar ta su, Yahaya Abdullahi ya bayyana cewa, an yi nazari sosai kan batutuwa daban-daban da ke fuskantar jam’iyyar tare da tabbatar da zaman lafiya gabanin babban taron jam’iyyar na kasa na ranar 26 ga Maris, 2022.