fidelitybank

Muna goyon bayan cire tallafin man fetur – Gwamnoni

Date:

Gwamnonin jihohin Najeriya, sun nuna goyon bayansu ga matakin da shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu da ya ɗauka na cire tallafin man fetur.

Gwamnonin sun bayyana haka ne a lokacin wata ganawa da suka yi da shugaban ƙasar a yau Laraba.

Wata sanarwa da ta fito ta hannun daraktan yaɗa labarai na fadar shugaban Najeriya, Abiodun Oladunjoye, ta ce gwamnonin sun rinƙa yin jawabi ɗaya bayan ɗaya a lokacin ganawar, inda suka rinƙa yaba wa shugaban ƙasar kan matakin da ya ɗauka.

Gwamnonin waɗanda suka je fadar bisa jagorancin shugaban ƙungiyar gwamnonin Najeriya kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq sun ce za su yi aiki tare da shugaban ƙasar wajen ganin an magance matsalolin da cire tallafin zai haifar.

Shugaba Bola Tinubu ne ya sanar da ƙarshen tallafin man fetur a ranar 29 ga watan Maris, lokacin da ya sha rantsuwar kama aiki.

Ya ce gwamnati za ta karkatar da kuɗaɗen tallafin zuwa ga wasu ɓangarori na ci gaban ƙasa.

Sai dai ƙungiyoyin ƙwadago na ƙasar sun nuna adawa da lamarin, inda suka yi yunƙurin shiga yajin aiki, amma daga baya an cimma matsaya bayan jerin tattaunawa tsakanin gwamnati da ƙungiyoyin na ƙwadago.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp