Wata kungiya mai suna Emefiele Mobilisation Team (EMT), ta ce Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) Dakta Godwin Emefiele, yana wakiltar wata dama ta musamman ta samar da zaman lafiya da hadin kai da ci gaba a kasar idan ya tsaya takarar shugaban kasa.
EMT kungiya ce, a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki.
Shugaban tawagar kuma kodineta na EMT na kasa, Dakta Jacob Attah, ya yi magana a wani taron manema labarai ranar Asabar a Lokoja a madadin kwamitin zartarwa na kungiyar na kasa.
A cewarsa, EMT ta kunshi ’yan kishin kasa ne da suka taru, domin nuna halayen shugabanin Gwamnan CBN.
“Ga mutumin da aka haifa a Kudu-maso-Yamma, ya yi karatu a Kudu maso Gabas, kuma daga Kudu maso Kudu, Dakta Emefiele yana wakiltar wata dama ta musamman ta zaman lafiya, hadin kai da ci gaba ba kawai a Kudancin Najeriya ba har ma a fadin Najeriya.
“Muna kira ga dukkan masu kishin kasa da su tashi tsaye, domin a lissafta su a cikin dukkan muhimman ayyuka na wanda zai zama shugaban Najeriya na gaba da kuma goyon bayan kiran da Dr. Godwin Ifeanyinchukwu Emefiele ya yi na ya tsaya takara mafi girma a kasarmu.