fidelitybank

Muna fatan ganin an samar da ingantaccen albashi – Kungiyar Gwamnoni

Date:

Kungiyar Gwamnoni ta NGF, ta ba da tabbacin cewa tattaunawar da ake yi tsakanin gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu da kungiyoyin kwadago za su haifar da ingantaccen albashi.

Da yake tashi daga taron da ta yi da sanyin safiyar ranar Alhamis, NGF a cikin wata sanarwa da shugabanta kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRazaq AbdulRahman ya fitar, ya ce sun amince da ci gaba da yin cudanya da masu ruwa da tsaki domin cimma matsaya mai kyau.

Batun mafi karancin albashi na kasa ya ci gaba da janyo ce-ce-ku-ce musamman bayan da Gwamnonin suka yi tazarce a kan Naira 62,000 da Gwamnatin Tarayya da masu zaman kansu suka bayar a kwamitin uku.

“Zauren ya samu bayani daga Ministar Harkokin Mata kan Bankin Duniya-Najeriya kan Matakan Ayyukan Mata, tare da sauran ayyukan ma’aikatar. Mambobin sun bayyana mahimmancin aikin tare da jaddada bukatar aiwatar da shi a matakin jiha kamar yadda aka tsara tun farko, kasancewar jihohi ne farkon fara aikin.

“Gwamnonin sun amince da aiki da gudummawar da ma’aikatar harkokin mata ke bayarwa wajen inganta daidaiton jinsi, karfafa mata, da kuma ci gaban zamantakewa a fadin Najeriya.

“Majalisar ta tattauna kan sabon mafi karancin albashi na kasa. Gwamnonin sun amince da ci gaba da yin cudanya da manyan masu ruwa da tsaki domin cimma matsaya mai dacewa. Mun ci gaba da sadaukar da kai ga tsarin kuma muna ba da tabbacin cewa za a samu mafi kyawun albashi daga tattaunawar da ake yi,” in ji sanarwar.

Gwamnonin sun kuma tattauna kan wasu batutuwan da suka shafi kasar nan, da suka hada da manufofin kasafin kudi da garambawul.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp