fidelitybank

Muna daf da rufe gidajen man fetur – IPMAN

Date:

Ƙungiyar dillalan man fetur masu zaman kansu ta ƙasa, (IPMAN), ta koka game da wasu matsaloli da dama da ‘ya’yanta ke fuskanta wajen samun man da suke sara daga kamfanin mai na ƙasar (NNPCL) su kai gidajen mansu musamman na yankin arewacin ƙasar.

Ƙungiyar ta ce wannan lamarin yana iya haifar da ƙarancin man har da ma rufe gidajen mai da dama.

Mataimakin shugaban ƙungiyar, Zarma Mustapha, ya shaida wa BBC cewa mafi yawan lokaci man fetur ɗin da suke samu daga NNPCL ba ya kai yawan da suke buƙata lamarin da ya sa suke siyan mai daga depo-depo masu zaman kansu kuma galibi sukan sayi man ne a kan farashi mai tsada wanda yake tasiri kan farashin da suke siyar da man a giajen mansu.

‘Muna cikin wani irin mawuyacin hali, musamman mu da ke arewacin Najeriya. A kudu suna iya ƙara karamar riba a kan farashinsu saboda suna samun sauƙi wurin ɗauko mai daga depo zuwa gidajen mansu. Amma mu da muke arewa ba mu iya samun mai a kan farashin da NNPCL take bayarwa daga depo masu zaman kansu, kuma idan zan dauki kayan nan sai na biya kuɗin mota, ga illolin kan hanya, ba karamin nauyi muke ɗauka ba.’ In ji shi.

Ya ƙara da cewa mafi yawan lokaci da kyar suke samun fita a harkokin kasuwanci nasu, kuma idan abubuwa suka ci gaba da tafiya a haka za a kai wani mataki da ba za su iya ci gaba da kasuwancin ba.

Ya ce:’ Idan ba a yi hankali ba, diloli masu zaman kansu za su kasa kasuwancin nasu, su rufe gidajen mansu saboda asara da ake yi da kuma rashin samun mai a kan farashin da ake bukata’.

Mataimakin shugaban kungiyar ya ce dole ne a dauki mataki cikin gaggawa idan har ana son su iya ci gaba da gudanar da harkokinsu.

‘Babban abin da ya kamata a yi shi ne NNPC ta yi ƙoƙarin bada mafi yawan man fetur din nan ga diloli masu zaman kansu kuma a farashin da ya kamata. Idan za a bayar da kaya ya kasance an bai wa IPMAN aƙalla kashi hamsin zuwa sittin, sai sauran a raba wa sauran dillalai saboda idan ka haɗa su ba su kai rabin gidajen man da muke da su ba,’ in ji shi.

Ya ce idan har ba a ɗauki matakan da suka kamata ba za a iya fuskantar matsanancin ƙarancin man fetur, musamman idan halin da ake ciki ya tilasta musu rufe gidajen mansu.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp