Jam’iyyar APC ta ce ba za ta yi kasa a gwiwa ba, wajen gudanar da shirye-shiryen babban taron kasa da za a gudanar a ranar 26 ga watan Maris.
Gwamna Mai Mala Buni na Yobe kuma shugaban kwamitin tsare-tsare na jam’iyyar APC mai rikon kwarya (CECPC) ya bayyana hakan a wata sanarwa da mai magana da yawunsa Mamman Mohammed ya fitar a Damaturu ranar Laraba.
“Muna ci gaba da kasancewa dangi guda daya, tare da mutunta shugabanmu da juna da kuma biyayya ga jam’iyyarmu,” in ji Mista Buni.
“Mun dukufa wajen ganin mun samu nasarar babban taron kasa mai zuwa, kuma ba za a karkatar da mu daga wannan kyakkyawar manufa ta ciyar da jam’iyyar APC gaba ba.”