fidelitybank

Muna da isassun bayanai dake nuna jami’an gwamnati na tattaunawa da ‘yan bindiga – Zamfara

Date:

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa gwamnatinsa na da isassun bayanai da ke tabbatar da cewa akwai wasu jami’an Gwamnatin Tarayya da ke jagorantar tattaunawar sirri da ƴan fashin daji a jihar.

Gwamnan ya faɗi hakan ne a wani martani da ya mayar wa Gwamnatin Tarayya, a yau Talata, bayan wata sanarwa da gwamnatin ta fitar a ranar Litinin tana ƙalubalantar gwamnan game da zargin da ya yi na cewa Gwamnatin Tarayya na tattaunawa da ƴan bindiga a jihar.

Sanarwar da ta fito daga ministan yaɗa labaru da wayar da kan al’umma na Najeriya, ta zargi gwamnan na Zamfara da sanya siyasa cikin harkar tsaro.

Sai dai a martanin da ya mayar ta hannun mai ba shi shawara kan yaɗa labaru, Bala Idris, gwamnan na Zamfara ya ce “muna da sahihan bayanai da shaidu game da abin da ya faru tsakanin wakilan gwamnatin tarayya da ƴan fashin daji a lokacin jerin tattaunawar da aka yi a wurare daban-daban a jihar Zamfara.”

Amma sanarwar ta ce gwamnatin Zamfara ba ta da niyyar fallasa sunayen wakilan Gwamnatin Tarayyar da suka yi tattaunawar a kafafen yaɗa labaru saboda girmama hukuma da kuma tsarin doka.

Haka nan gwamnatin jihar ta soki lamirin ministan yaɗa labarun na Najeriya kan martanin da ya mayar mata a ranar Litinin, inda ta ce ya yi hakan ne ba tare da yin binciken da ya dace ba.

Ita dai gwamnatin Zamfara ta ce an gudanar da tattaunawar da ta yi magana a kai ne a yankunan Birnin Magji da Maradun da Mun Haye da Ajah da Bawo da kuma Bagege.

A martanin na ranar Talata, gwamnatin Zamfara ta ce “Tattaunawa da ƴan bindiga babban kuskure ne wanda ba za ta so ta aikata ba, kuma hakan ba zai kawo ƙarshen matsalar ba, face ma, ya ƙara ƙarfafa wa ƴan fashin gwiwa.”

A ranar Litinin ne dai Gwamnatin Tarayya a cikin sanarwar da ta fitar ta ce “Babu wani jami’in gwamnatin Tarayya da ke tattaunawa da wani ɗan bindiga ko ƙungiyar ƴan bindiga.”

“Sai dai gwamnatin a shirye take ta yi amfani da duk wata hanya wajen sassauta yanayi na tashin hankali da ake ciki da kuma mayar da zaman lafiya a yankunan da ƴan fashin daji suka addaba.”

Zamfara dai na a sahun gaba cikin jihohin arewa maso yammacin Najeriya da matsalar rashin tsaro ta ƴan fashin daji ke ci gaba da yi wa illa.

Ko a makon da ya gabata, ƴan daji sun kai hari a gidajen kwanan ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau, inda suka yi awon-gaba da ɗalibai da dama, waɗanda har yanzu wasu daga cikin su ke hannun ƴan fashin.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp